Home Labaru Garkuwa Da Mutane: Majalisar Dattawa Ta Gayyaci Shugaban ‘Yan Sandan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane: Majalisar Dattawa Ta Gayyaci Shugaban ‘Yan Sandan Nijeriya

270
0

Majalisar dattawa ta bukaci shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya Muhammadu Adamu ya bayyana gaban ta, domin jin ta bakin sa game da yadda ta’addancin masu garkuwa da Mutane ke ci-gaba da kamari a fadin Nijeriya.

An dai gayyaci Muhammadu Adamu ne domin samun masaniya tare da kulla dabaru da shawarwarin kawo karshen ta’addancin garkuwa da mutane a Nijeriya.

Majalisar, ta yanke shawarar gayyatar shugaban ‘yan sandan ne, biyo bayan kudirin da Sanata Shehu Sani ya gabatar.

Bayan tattaunawa a kan batutuwan ta’addancin masu garkuwa da mutane, musamman a yankunan jihar Kaduna, majalisar ta yanke shawarar gayyatar shugaban ‘yan sandan domin daura damarar dasa aya a kan wannan mummunan kalubale.

Yayin tafka muhawara a zauren majalisar, Sanata Shehu Sani ya ce, ta’addancin masu garkuwa da kashe-kashen al’umma baya ga kone gidaje a wasu kauyukan jihar Kaduna, ya kai intaha da kawo yanzu an gaza gane bakin zaren.

Leave a Reply