Home Labaru Garambawul: Majalisar Dattawa Ta Amince Da Sauya Ranar Dimokuradiya A Najeriya

Garambawul: Majalisar Dattawa Ta Amince Da Sauya Ranar Dimokuradiya A Najeriya

360
0
Majalisar Dattawa

Majalisar Dattawa ta amince da dokar da ta tsaida ranar 12 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin sabuwar ranar dimokuradiyya sabanin yadda yake ranar 29 ga watan Mayu a baya.

Matakin majalisar na zuwa ne bayan akalla shekara guda da shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana sauya ranar Dimokuradiyar ta Najeriya.

A zaman da ta yi majalisar ta dattawa ta sanya hannu kan wannan kudiri, wanda majalisar wakilai ta amince da shi tun a watan Disambar shekarar 2018. A zaman bisa jagorancin mataimakin shugaban majalisar, Ike Ekweremadu, majalisar ta yi amanna da sabon kudirin, yayin da shugaban masu rinjaye, Ahmed Lawal, ya yi fashin baki kan manufar shugaban kasa.