Home Labaru Kula Da Lafiya: Majalisar Dattawa Ta Shigar Da Kudirin Inshora A Cikin...

Kula Da Lafiya: Majalisar Dattawa Ta Shigar Da Kudirin Inshora A Cikin Dokar Kasa

182
0

Majalisar dattawan ta amincewa da shigar da kudirin inshorar lafiya na shekara ta 2019 a  cikin doka.

Majalisar ta shigar da kudirin inshorar lafiya ne bayan bincike a kan kudirin da kwamitin majalisar mai kula da harkokin lafiya ya gudanar, a karkashin jagorancin Sanata Lanre Tejuoso na jam’iyyar PDP mai wakiltan Ogun ta tsakiya.

A lokacin zaman majalisar,shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki,  ya buga sandar iko akan sabon kudirin bayan an karanta  shi sau uku a majalisar.

Kazalika majalisar ta sake shigar da sabon kudirin hukumar ‘yan sanda mai lamba 683 cikin dokar kasa, bayan kwamitin kula da harkokin ‘yan sanda ya gabatar da sakamakon binciken sa a karkashin jagorancin Sanata Tijjani Kaura na jam’iyyar APC mai wakiltan Zamfara ta arewa.

Leave a Reply