Home Labaru An Nada Dahiru Ahmed A Matsayin Mai Taimaka Wa Uba Sani A...

An Nada Dahiru Ahmed A Matsayin Mai Taimaka Wa Uba Sani A Kan Harkar Yada Labarai

109
0

An bayyana nadin da sabon Gwamnan jihar Kaduna Sanata
Uba Sani ya yi wa mataimakain shugaban gidan rediyo da
talabijin na Liberty da ke Kaduna Dahiru Ahmed a matsayin
mafi mahimmanci daga cikin sabbin nade-naden da sabon
gwamnan yi.

Gwamna Uba Sani dai ya nada Dahiru Ahmed ne a matsayin Babban Mai ba shi shawara a kan harkokin gidajen rediyo da talabijin.

Idan dai ba a manta ba, Dahiru Ahmed ya kasance daya daga cikin amintattun ‘yan jaridar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa’i ay yi aiki da su a harkokin yada labarai.

Yayin da ya ke karbar sakonnin fatan alheri daga masoya da abokan arziki, Dahiru Ahmed ya bayyana nadin a matsayin hukuncin Allah domin bai nema ba, ya na mai mika godiya da fatan Allah ya fidda shi kunyar gwamnati da daukacin al’ummar jihar Kaduna.

Leave a Reply