Home Labaru Korafin Zabe: Shari’ar Shehu Sani Da Uba Sani Zuwa Sai Ran 25...

Korafin Zabe: Shari’ar Shehu Sani Da Uba Sani Zuwa Sai Ran 25 Ga Yuli

480
0

Kotun sauraren korafe-korafen zabe da ke a Kaduna, ta dage zaman ta zuwa ranar 25 ga watan Yuli na shekara ta 2019, domin sauraren jawabin karshe daga bakin lauyoyi a shari’ar Sanata Shehu Sani da Sanata Uba Sani.

Sanata Shehu Sani dai ya na kalubalantar nasarar da Uba Sani ya samu a zaben da ya gabata, inda ya bukaci kotu ta tabbatar da shi a matsayin wanda ya lashe zaben.

Sanata Shehu Sani yayin da yake magana da manema labarai bayan ganawar su da Adams Osiomhole a Sakatariyar APC a Abuja (26-July-2018)/APC Publicity Unit

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan zaman kotun, lauyan sanata Shehu Sani Morris A. Odeh, ya ce an gama sauraren shaidu saboda sanata Uba Sani ya kasa gabatar da shaida ko guda.

Odeh ya kara da cewa, sanata Shehu Sani ya gabatar da shaidu biyu a lokacin da ake sauraren shari’ar, amma sanata Uba sani ya gaza gabatar da shaida ko guda.

Ya ce abin da ake ciki yanzu shi ne, za su koma ranar 25 ga watan Yuli don su gabatar da jawabin karshe, daga nan su saurari hukuncin kotu.

Leave a Reply