Home Labaru Hukumar INEC Za Ta Kirkiro Rumfunan Zabe Tare Da Gyaran Mazabu

Hukumar INEC Za Ta Kirkiro Rumfunan Zabe Tare Da Gyaran Mazabu

389
0
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta kasa, INEC
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta kasa, INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC, ta ce a cikin watanni hudun farko na shekara ta 2020, za ta kara kirkiro wasu rumfunan zabe tare da yi wa mazabu gyara a fadin Nijeriya.

Kwamishinan Zabe na Tarayya kuma Jami’in Wayar da Kan Jama’a Festus Okoye ya bayyana haka, yayin da ya ke jawabi a wajen wani taro da hukumar ta yi da Kungiyoyin Rajin Kare Dimokradiyya da Sa-ido kan Zabe a Abuja.

Okoye, ya ce hukumar zabe za ta tuntubi dukkan bangarorin da ke da ruwa da tsaki domin jin ta bakin su game da karin rumfunan zaben da za a yi, ya na mai cewa akwai rumfunan zabe dubu 119 da 973 da kuma wuraren zabe dubu 57 da 73 a fadin Nijeriya.

Ya ce hukumar za ta hada kai da Majalisar Dattawa da ofishin Atoni Janar na Nijeriya domin samun maslahar yadda za a tsara karin da kuma gyaran su ta yadda za su shiga cikin doka.

Leave a Reply