Home Labaru Labarun Ketare Kofin Duniya: FIFA Ta Ba Sa’udiyya Izinin Shirya Gasar 2034

Kofin Duniya: FIFA Ta Ba Sa’udiyya Izinin Shirya Gasar 2034

59
0
R (4)
R (4)

Hukumar ƙwallon kafa ta duniya, Fifa ta bai wa Saudi Arabia damar gudanar da gasar cin kofin duniya a 2034 a babban taron da ta yi ranar Laraba.

Haka kuma hukumar ta tabbatar da cewar Sifaniya da Portugal da Morocco za su shirya wasannin da za a yi a 2030 a babbar gasar tamaula ta duniya.

Gasar kofin duniya da za a yi a 2030 za a yi wasu wasannin a Argentina da Paraguay da Uruguay, domin bikin shekara 100 da fara gasar.

An amince da wannan hukuncin bayan kaɗa kuri’a da aka gudanar a babbar taron hukumar ƙwallon kafa ta duniya da ta yi ranar Laraba.

Leave a Reply