Tsohon gwamnan jihar Bauchi Mohammed Abubakar, ya amsa bayyana ma wata babbar kotun tarayya da ke Abuja cewa ya kashe naira biliyan 8 da rabi ana saura kwanaki biyu kacal ya mika mulki.
Sai dai ya shaida wa kotun cewa, ya kashe kudaden ne domin biyan wasu kamfanoni da su ka yi kwangiloli a jihar lokacin ya na kan mulki.
Ya ce ya biya kamfanonin adadin kudaden ne a ranar da jihar Bauchi ta same su daga babban bankin Nijeriya CBN, a matsayin biyan bashin ayyukan gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar ta yi.
Tsohon
gwamnan ya bayyana haka ne ta bakin lauyan sa Basil Kpenkpen, a cikin wata
takarda da ya mika wa kotun domin kare kan sa daga tuhumar badakalar naira biliyan
19 da miliyan 900 da hukumar EFCC ke yi ma shi.
You must log in to post a comment.