Home Labarai Saka Hannu: Gundogan Ya Koma Manchester City

Saka Hannu: Gundogan Ya Koma Manchester City

310
0
1724410801001 472e28b5 d8eb 4d8a 9f7d da5e6459d856
1724410801001 472e28b5 d8eb 4d8a 9f7d da5e6459d856

Ɗan ƙwallon Jamus, Ikay Gundogan ya sake komawa Manchester City, inda ya saka hannu a kwantiragin shekara guda.

Ɗan wasan ya dawo ƙungiyar, da ke riƙe da kofin Premier , kimanin wata 12 baya barin ƙungiyar.

Gundogan ya kwashe shekara bakwai a Manchester City, inda ya lashe kofuna da dama, har ya kai ga zama kyaftin ɗin ƙungiyar.

Ya kwatanta lokacin sa a Manchester City a matsayin lokacin farin ciki, sannan ya ce ya ƙagu ya ci gaba taka leda a ƙungiyar.

Gundogan na cikin ƴan wasan da suka fi ɗaukar albashi a Barcelona, wanda tafiyar sa zai taimaka wa ƙungiyar wajen daidaita kashe kuɗin su domin gudun karya doka.

Leave a Reply