Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Saka Hannu: Gundogan Ya Koma Manchester City

1724410801001 472e28b5 d8eb 4d8a 9f7d da5e6459d856

1724410801001 472e28b5 d8eb 4d8a 9f7d da5e6459d856

Ɗan ƙwallon Jamus, Ikay Gundogan ya sake komawa Manchester City, inda ya saka hannu a kwantiragin shekara guda.

Ɗan wasan ya dawo ƙungiyar, da ke riƙe da kofin Premier , kimanin wata 12 baya barin ƙungiyar.

Gundogan ya kwashe shekara bakwai a Manchester City, inda ya lashe kofuna da dama, har ya kai ga zama kyaftin ɗin ƙungiyar.

Ya kwatanta lokacin sa a Manchester City a matsayin lokacin farin ciki, sannan ya ce ya ƙagu ya ci gaba taka leda a ƙungiyar.

Gundogan na cikin ƴan wasan da suka fi ɗaukar albashi a Barcelona, wanda tafiyar sa zai taimaka wa ƙungiyar wajen daidaita kashe kuɗin su domin gudun karya doka.

Exit mobile version