Kungiyar dattawan arewa ta sake sabonta kiran da take yi na
neman Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi murabus.
A lokacin da yake magana da manema labarai, mai magana da
yawun kungiyar Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya ce hujjojin da ke
kasa sun marawa kiraye-kiraye da suke yi ga shugaban kasa ya
yi murabus a baya.
Ya ce shugaban kasa ya yi rantsuwa da Al-Qur’ani domin kare
al’umman Najeriya, amma ya gaza yin hakan, kuma wannan shi
ne shekarar sa ta biyar akan mulki.
Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya kara da cewar halin da ake ciki ya
na kara tabarbarewa a karkashinsa kuma babu alama da ke nuna
abubuwa za su inganta.
Kungiyar ta ce rayuwa a karkashin wannan gwamnati ba ta da
wani tasiri, inda ta ce abinda ake bukata da shugaban da ya rasa
mafita shi ne ya yi murabus.
You must log in to post a comment.