Home Labaru Majalisa Ta Mika Wa Shugaba Buhari Kasafin Kudin 2022

Majalisa Ta Mika Wa Shugaba Buhari Kasafin Kudin 2022

286
0

Majalisar Dokokin Tarayya ta mika wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari kasafin kudin kasar na badi domin ya rattaba hannu a kai.

Wata majiya daga ofishin Magatakardan Majalisar da ta tabbatar da hakan, ta ce an mika wa shugaban kasar kasafin kudin ne tun a ranar Lahadi, 26 ga watan Disamban 2021.

A cewar majiyar, ana sa ran Shugaba Buhari zai rattaba hannu kan kasafin kudin kafin ranar 31 ga watan Disamban 2021, a yayin da za a yi bankwana na karshe da shekarar.

Tun a ranar Lahadi, 26 ga wata aka mika wa shugaban kasa kasafin kudin.

Majiyar ta kuma karyata rade-radin da suka rika yaduwa a bayan nan cewa ba a aike wa shugaban kasa kasafin kudin ba yayin da ya rage kwanaki uku a yi bankwana da shekarar 2021.

Ana iya tuna cewa, a makon jiya ne zauren Majalisun Tarayya biyu da suka hada da na Wakilai da Dattawa suka amince da kasafin kudin na badi gabanin su tafi hutun su na karshen shekara.

Leave a Reply