Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya taya Donald Trump murna, inda ya ce a shirye yake su ci gaba da aiki tare domin inganta alaƙa tsakanin Najeriya da Amurka.
Mai taimakawa shugaban kasan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya ce, idan suka haɗa kai, za su inganta tattalin arziki da zaman lafiya da magance matsalolin da al’umma ke fuskanta.
Tinubu ya kuma yaba wa Amurkawa bisa yadda suka gudanar da zaɓen cikin lumana.
Tinubu ya ce kasancewar Trump ya taɓa yin mulkin ƙasar, dawowar sa a matsayin shugaban ƙasar na 47 zai zo da gagarumar sauyi a tattalin arziki da ƙarin haɗin kai tsakanin Amurka da ƙasashen Afirka.
Trump ne dai ya sanar da samun nasarar sa a jawabin sa ga magoya bayan sa, inda ya ce ya samu gagarumar nasara.














































