Home Labaru Karbo Kudade: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Kalubalantar Hukuncin Kotun Burtaniya

Karbo Kudade: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Kalubalantar Hukuncin Kotun Burtaniya

305
0

Gwamnatin tarayya ta fara shirye-shiryen kalubalantar hukuncin da kotu ta yanke na kwace kadarorin najeriya da ya kai na dala billiyan 9.

Mai Shari’a Butcher na kotun kula da harkokin hada-hadar kudade na kasar Burtaniya ya yanke hukuncin a karar da wasu kamfanoni suka shigar.

Mai Shari’a Butcher

Jim kadan bayan yanke hukuncin wanda yaba kamfanonin nasara, gwamnatin tarayya ta sha alwashin daukaka kara, wanda take ganin ba a yi mata adalci ba.

A cikin wata sanarwa da ta fito ta ma’aikatar kula da harkokin shari’a, ta ce tuni ta bukaci lauyoyinta su kafa kwamitin daukaka kara akan hukuncin da kotun ta yanke.

Leave a Reply