Home Labaru Diflomasiyya: An Sake Kashe Wani Dan Nijeriya A Afrika Ta Kudu

Diflomasiyya: An Sake Kashe Wani Dan Nijeriya A Afrika Ta Kudu

229
0

Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna Afrika ta kudu, ta ce an sake kashe wani dan Nijeriya mai suna Tony Elechukwu, lokacin da wani dan bindiga ya dirka masa harsashi a yankin Witbank Mpumalanga.

Shugaban ‘yan Najeriya mazauna kasar Ben Okoli ya tabbatar da aukuwar lamarin, a cikin wata wasika da ya aike wa ofishin Jakadancin Nijeriya a Johannesburg.

Okoli, ya ce wannan shi ne karo na uku da ake kashe ‘yan Nijeriya a cikin wannan watan, bayan wadanda aka kashe a ranakun 6 da kuma 9 ga wannan watan.