Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Diflomasiyya: An Sake Kashe Wani Dan Nijeriya A Afrika Ta Kudu

Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna Afrika ta kudu, ta ce an sake kashe wani dan Nijeriya mai suna Tony Elechukwu, lokacin da wani dan bindiga ya dirka masa harsashi a yankin Witbank Mpumalanga.

Shugaban ‘yan Najeriya mazauna kasar Ben Okoli ya tabbatar da aukuwar lamarin, a cikin wata wasika da ya aike wa ofishin Jakadancin Nijeriya a Johannesburg.

Okoli, ya ce wannan shi ne karo na uku da ake kashe ‘yan Nijeriya a cikin wannan watan, bayan wadanda aka kashe a ranakun 6 da kuma 9 ga wannan watan.

Exit mobile version