Home Labaru Ilimi Bude Makarantu: Kungiyar ASUU Ta Yabawa Matakin Gwamnatin Tarayya

Bude Makarantu: Kungiyar ASUU Ta Yabawa Matakin Gwamnatin Tarayya

705
0

Kungiyar malamai ta ASUU ta goyi bayan shawarar da gwamnatin tarayya ta yanke na dakatar da daliban aji shida daga za na jarrabawar WAEC da aka shirya farawa a ranar 4 ga watan Agusta.

Kungiyar ta shawarci gwamnatin tarayya da ta bar makarantu a rufe har zuwa shekarar 2021 domin tabbatar da ingantaccen shiri kafin a sake buɗe su.

Kungiyar ASUU ta buga misali da hukuncin da gwamnatin kasar Kenya ta yanke na cewa kafatanin makarantu a kasar za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai shekara mai zuwa.

A wata hira da shugaban ASUU na kasa, Farfesa Biodun Ogunyemi, ya yi da manema labarai ya ce kar a kuskura a yi sakaci da lafiyar dalibai.

Farfesa Ogunyemi,  ya ce kada a sake a buɗe makarantu har sai gwamnatin tarayya ta samu yarjewa ta iyayen yara kuma sun nuna amincewarsu a kan hakan.

Leave a Reply