Hukumar tsaro ta farin kaya DSS, ta ce za ta bi umurnin kotu na ba Sheikh Ibrahim El-Zakzaky damar tafiya kasar waje domin samun kulawar likitoci.
Idan dai ba a manta ba, a safiyar Litinin da ta gabata ne, babbar kotun jihar Kaduna ta ba El-Zakzakky da matar sa Zeenat beli domin zuwa neman magani a kasar waje.
Da ya ke yanke hukunci, mai shari’a Darius Kobo ya yi umurnin cewa, jami’an gwamnatin jihar Kaduna su yi wa El-Zakzaky rakiya zuwa kasar waje.
A
cikin wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Litinin da ta gabata, kakakin
hukumar Peter Afunnaya, ya ce kamar yadda ya ke a tsarin hukumar za ta bi
umurnin kotun.
You must log in to post a comment.