Home Coronavirus Annoba: Cutar Korona Ta Kama Mutum 110 A Najeriya

Annoba: Cutar Korona Ta Kama Mutum 110 A Najeriya

84
0
Hukumar ɗakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 110 da suka kamu da cutar korona a Najeriya.

Hukumar ɗakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 110 da suka kamu da cutar korona a Najeriya.

Alƙalumman sun nuna mutum 27 suka kamu da cutar a jihar Imo sai a jihar Katsina da aka samu mutum 23 a ranar Lahadi.

Sauran sun hada da jihar Rivers inda aka samu mutum 20, sai jihar Ondo mai mutum 11.

Hukumar tace a jihar Kaduna ma an samu ƙarin mutum 9 da suka kamu da cutar.

Ya zuwa dai yanzu dai jimillar mutum 214,092 suka kamu da cutar a Najeriya yayinda 207,254 suka warke mutum 2,976 suka rasa rayukan su.