Shugaban hukumar kula da harkokin shige da fice na Najeriya NIS Muhammad Babandede, ya kawo wata ziyarar aiki ta yini daya zuwa ofishin hukumar dake Kaduna, a kokarin sa na tabbatar da dorewar nasarar da hukumar ke samu wajen zamanantar da ayyukan ta.
Yayin ziyarar, Muhammad Babandede, ya kuma ziyarci gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, a fadar gwamnatin jihar ta Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.
Ya yaba wa gwamna Nasiru El-Rufai bisa goyon bayan da yake ba hukumar sa a jihar da kuma samar da kyakkyawan yanayi na gudanar da aikace-aikacen ta wajen bunkasa hada-hadar kasuwanci a Kaduna da tabbatar da dorewar zaman lafiya.
A nashi bangaren, gwamna El-Rufai, ya taya Shugaban na NIS, murna kan dimbin ci gaban da ya samar a cikin shekara uku na shugabancin sa, da kuma kokarin da yake wajen kawo sauye-sauye masu ma’ana a hukumar.