Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tafi Birtaniya bayan ya kammala ziyara a birnin Maiduguri na jihar Borno a yau.
Mai maitamakawa shugaban kasa a kafafen yada labarai, Femi Adesina, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja.
Ana sa ran shugaban kasa zai kaddamar da wasu ayyukan ci gaban al’umma musamman a bangaren ilimi da kiwon lafiya da kuma hanyoyi a ziyarar da zai kai jihar Borno.
Wasu rahotanni sun nuna cewar a lokacin ziyarar shugaban kasa a London, zai yi nazari game da sabbin ministocin da zai yi aiki da su a sabuwar gwamnatin sa. Rahotannin sun bayyana cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari zai dawo Najeriya ne a ranar 5 ga watan Mayu.
You must log in to post a comment.