Ministan harkokin yankin Neja Delta, Godswill Akpabio, ya yi zargin cewa ‘yan majalisar tarayya sun taka rawar gani wurin rikicin kudi da hukumar ta shiga inda yace da yawa daga cikin kwangilar da aka fitar a hukumar, duk ‘yan majalisar aka bai wa

Tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom ya fuskanci ‘yan kwamitin majalisar wakilai domin amsa tambayoyi kan ma’aikatar harkokin Neja Delta, ya ce da yawa daga cikin kwangilar da hukumar kula da ci gaban yankin Neja Delta (NDDC) ta fitar duk ta bai wa ‘yan majalisar tarayya ne














































