Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon shugaban Karamar Hukumar Olamaboro ta Jihar Kogi Isaac Emmanuel Ekpa.
Makusantantan sa sun bayyana cewa an dauke shi ne ranar Juma’a a Ochadamu ta Karamar Hukumar Ofu a lokacin da yake komawa gida.
Rahotanni sun ruwaito cewa Ekpa na shirin birne mahaifin sa ne bayan ya rasu a lokacin da lamarin ya faru.
Kafafen yada labarai a Najeriya sun ruwaito kakakin rundunar ‘yan sandan Kogi, Williams Ayah, na cewa wasu ‘yan sandan sintiri ne suka tsinci mota babu kowa cikin ta a kan titin Ochadamu.
Bayan sun bincika motar ne kuma suka tsinci katin shaida mai dauke da sunan Emmanuel Isaac Ekpa, a cewar sa.
Rahotanni na cewa masu garkuwar sun nemi a biya su kudin fansa naira miliyan 25, inda aka ce wani dan uwan sa na tattaunawa da su domin neman ragi kan abin da suka nema.
You must log in to post a comment.