Kudurin dokar kirkirar sabbin masarautu ya tsallake karatu na farko a majalisar dokoki ta jihar kano.
Majalisar dai ta soma zaman nazari ne a kan takardar da aka shigar a gaban ta ta neman kirkirar sabbin masarautu hudu a fadin jihar.
Rahotanni sun ce, majalisar ta na kokarin yi wa dokar masarautar ta shekara ta 1984 kwaskwarima ne, bayan bukatar da ta ce wasu kungiyoyi sun shigar gaban ta a kan neman sake kirkirar masarautu a Jihar.
Sai dai tun kafin a fara zaman majalisar, mutanen kananan hukumomin garuruwan da za a daga hakiman su, sun yi wa majalisar dafifi da zummar nuna goyon bayan su ga majalisar bisa yunkurin da ta ke yi.
You must log in to post a comment.