Gwamnatin tarayya tace nan gaba kadan Jirgin kasan da zai rika jigila a cikin Babban Birnin Tarayya Abuja domin rage wahalar zirga-zirga.
Ministan Abuja, Malam Muhammadu Bello ne ya bayyana hakan yayin da ya kai ziyara Kamfanin CCECC da ke kwagilar aikin jirgin.
A yayin ziyarar an zagaya da ministan da ayarinsa lungu da sako na cibiyar gudanar ayyuka da kuma sarrafa jirgin da ke Idu.
A jawabin Babban Sakataren Hukumar FCTA Mista Olusade Adesola ya ce, makasudin ziyarar shi ne, su duba inda aka kwana a aikin jirgin da kuma inda za a dora.
Adesola ya ce hukumar ta kashe kudi mai yawa, da kuma tallafin Gwamnatin Tarayya har an kai ga matakin soma gwajin jirgin kafin annobar COVID-19 ta bulla, lamarin da ya ta tilasta dakatar da aikin.
Dangane da batun tsaro, Babban sakataren yace an tanadin cikakken tsarin tsaro ga jirgin tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro na birnin.














































