Home Home Shugaba Buhari Ya Jajantawa Al’ummar Kano Kan Hatsarin Kwale-Kwale A Bagwai

Shugaba Buhari Ya Jajantawa Al’ummar Kano Kan Hatsarin Kwale-Kwale A Bagwai

105
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajanta wa Al’ummar Jihar Kano da kuma gwamnatin jihar bisa hatsarin kwale-kwalen da ya auku a Ƙaramar Hukumar Bagwai inda fiye da mutum 20 suka rasa rayukan su.


A wani saƙo da ya aike wa gwamnatin da jama’ar jihar, shugaba
Buhari ya ce hukumomin gwamnatin tarayya za su bayar da
gudunmawar da ta dace a daidai lokacin da ake ci gaba da
neman waɗanda suka ɓace yayin hadarin.


A ranar Talatar da ta gabata ne dai kwale-kwalen ya nutse dauke
da fasinjojin yawancin su yara ƙanana kuma ɗaliban Islamiyya.


Jami’an ƴan sanda da ƴan kwana-kwana da masunta ne ke ci
gaba da aikin ceton wadanda suka saura da nunfashi da kuma
gawawwaki.