Fadar masarautar Katsina ta fitar da wata sanarwar, sakon jaje ga daukacin jama’arta kan ibtila’in kashe-kashen da mutanen gundumomin Batsari, da Dan-Musa, da Kankara da Wagini da sauransu wuraren da abun ya shafa suka samu kansu a ciki.
Sakataren masarautar Bello M Ifo shi ne ya fitar da ita, tare da shaida wa jama’a cewa sakamakon halin da suka samu kansu a ciki na alhini da jimami.
A wannan karon masarautar ta yanke shawarar a wannan karon ba za a yi hawan Sallah ba kamar yadda aka saba a baya.
Bello ya ce Mai-martaba sarkin Katsina Abdulmumin Kabir Usman, da majalisar masarautar ne suka ga dacewar dage duk wasu shagulgula don nuna alhini kan abin da ya samu jama’arsu.
A karshen sanarwar ta ce za a je sallar idi kamar yadda aka saba, da yin addu’o’in neman zaman lafiya ga jihar Katsina da Najeriya baki daya.
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.














































