Home Labaru NDLEA Ta Kama Fitattun Mawakan Gambara Biyu Da Tabar Wiwi A Lagos

NDLEA Ta Kama Fitattun Mawakan Gambara Biyu Da Tabar Wiwi A Lagos

433
0

Jami’an Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, sun kama wasu fitattun mawaka biyu da wasu mutane hudu dauke da kwayoyi a wani samame da su ka kai a birnin Legas.

Hukumar ta shaida wa manema labarai cewa, an samu wasu nau’ukan tabar wiwi a hannun mawakan, wadanda su ka hada da Zinoleesky da Mohbad da wasu mutane hudu da ake zargi.

Mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi, ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan an gama bincike.

Mohbad da Zinoleesky dai shahararrun mawakan Gambara ne na zamani, wadanda ake fitar da wakokin su a fadin nahiyar Afrika da ma duniya baki daya.

Leave a Reply