Home Labarai Mutum Fiye Da Dubu Tamanin Ne Suka Shiga Najeriya Don Gudun Hijira

Mutum Fiye Da Dubu Tamanin Ne Suka Shiga Najeriya Don Gudun Hijira

345
0
In this photo taken on September 15, 2016 women and children queue to enter one of the Unicef nutrition clinics at the Muna makeshift camp which houses more than 16,000 IDPs (internaly displaced people) on the outskirts of Maiduguri, Borno State, northeastern Nigeria. Aid agencies have long warned about the risk of food shortages in northeast Nigeria because of the conflict, which has killed at least 20,000 since 2009 and left more than 2.6 million homeless. In July, the United Nations said nearly 250,000 children under five could suffer from severe acute malnutrition this year in Borno state alone and one in five -- some 50,000 -- could die. / AFP PHOTO / STEFAN HEUNIS

Hukumomi a Nijeriya, sun ce sama da mutane dubu tamanin ne su ka shigo daga kasashen waje a matsayin ‘yan gudun hijira.

Shugabar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Nijeriya Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta bayyana haka, yayin da ake bikin tunawa da Ranar ‘Yan Gudun Hijira ta Duniya.

Hajiya Imaan ta kara da cewa, mutanen da su ka shigo Nijeriya sun fito ne daga kasashe talatin da hudu, kuma wadanda su ka yi rajista kusan dubu tamanin da hudu ne.

Ta ce Mutanen da su ka fi shigowa Nijeriya sun fito ne daga Kudancin Kamaru saboda ana rikici a yankin Ambazonia.

Hajiya Imaan ta cigaba da cewa, gwamnatin Nijeriya ta na ware makudan kudade domin tallafa wa ‘yan gudun hijirar kamar yadda dokokin kasashen duniya su ka bukata, kuma ‘yan gudun hijirar su na da zabi uku, ko dai su cigaba da zama a Nijeriya, ko kuma su koma kasashen su idan sun gamsu da yanayin da ake ciki a can, ko kuma Najeriya ta kai su wasu kasashen.

Leave a Reply