Home Home Muric Ta Bukaci Tinubu Ya Ba Musulmai Mukaman Minista Fiye Da Kiristoci

Muric Ta Bukaci Tinubu Ya Ba Musulmai Mukaman Minista Fiye Da Kiristoci

87
0

Kungiyar kare hakkin Musulmai ta Nijeriya MURIC, ta bukaci zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba musulmai mukaman ministoci fiye da Kiristoci idan aka rantsar da shi.

A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar Farfesa Ishaq Akintola ya fitar, ya ce gwamnatoci da dama sun maida Musulmai tamkar saniyar ware a rabon mukaman gwamnati.

Ya ce akwai jihohi a shiyyoyin da musulmai su ka fi rinjaye musamman shiyyoyi masu jihohi shida, don haka ya kamata a ba Musulmai ministoci hudu sannan Kiristoci su dauki guda biyu domin samun daidaito.

Farfesa Ishaq Akintola, ya ba da misalan da jihohin Taraba da Adamawa da Bauchi a yankin Arewa maso Gabas, sai kuma jihohin Nasarawa Kogi da Neja a yankin Arewa taTsakiya, da kuma Oyo da Osun da Ogun da Lagos a Kudu maso Yamma da kuma jihar Kaduna a yankin Arewa maso Yamma.

Kungiyar, ta bayyana yadda gwamnatoci da dama su ka nuna wa Musulmai wariya duk da rinjayen da su ke da shi a wadannan yankunan, inda ta ce a jihohin Borno da Katsina da Sokoto kadai ne ake kula da hakkin Musulmai a lamurran gwamnati.

Leave a Reply