Home Labaru Mulki: Falana Ya Zargi Buhari Da Burin Neman Tazarce

Mulki: Falana Ya Zargi Buhari Da Burin Neman Tazarce

388
0
Femi Falana, Fitaccen Mai Rajin Kare Hakkin Bil-Adama
Femi Falana, Fitaccen Mai Rajin Kare Hakkin Bil-Adama

Fitaccen mai rajin kare hakkin bil-Adama, Femi Falana, ya ce yadda gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke kuntata wa ‘yan jarida manuniya ce ta shirin neman zarcewa a kan mulki karo na uku.

Falana ya bayyana haka ne, yayin da ya ke gabatar da kasida a wajen taron kaddamar da wani littafi mai taken ‘Testimony to courage’ a Turance, wanda aka wallafa a kan shugaban kamfanin jaridar Premium Times Dapo Olorunyomi, a jihar Legas.

Ya ce Nijeriya na cikin mawuyacin hali, don haka bai kamata kafafen yada labarai su yi shiru ba, kuma nan ba da jimawa ba watakila a fara jin an fara kokarin neman tazarce karo na uku.

Lauyan ya kara da cewa, ba za su bari a lalata kafafen yada labarai ba, kuma babu wani mai mulkin kama karya da ya isa ya danne ‘yan Najeriya.

A karshe ya bayyana damuwar sa da yadda Alkalin babbar kotun tarayya da ke a Legas mai shari Ijeoma Ojukwu ke gudanar da shari’ar Omoyele Sowore, inda ya ce bai taba ganin irin sharuddan belin da ta gindaya ma shi ba.