Fitaccen mai rajin kare hakkin bil-Adama, Femi Falana, ya ce yadda gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke kuntata wa ‘yan jarida manuniya ce ta shirin neman zarcewa a kan mulki karo na uku.
Falana ya bayyana haka ne, yayin da ya ke gabatar da kasida a wajen taron kaddamar da wani littafi mai taken ‘Testimony to courage’ a Turance, wanda aka wallafa a kan shugaban kamfanin jaridar Premium Times Dapo Olorunyomi, a jihar Legas.
Ya ce Nijeriya na cikin mawuyacin hali, don haka bai kamata kafafen yada labarai su yi shiru ba, kuma nan ba da jimawa ba watakila a fara jin an fara kokarin neman tazarce karo na uku.
Lauyan ya kara da cewa, ba za su bari a lalata kafafen yada labarai ba, kuma babu wani mai mulkin kama karya da ya isa ya danne ‘yan Najeriya.
A
karshe ya bayyana damuwar sa da yadda Alkalin babbar kotun tarayya da ke a
Legas mai shari Ijeoma Ojukwu ke gudanar da shari’ar Omoyele Sowore, inda ya ce
bai taba ganin irin sharuddan belin da ta gindaya ma shi ba.
You must log in to post a comment.