Mai ba shugaban kasa shawara ta fuskar tsaro Babagana Mungono, ya ce ana shigo da muggan makamai ta iyakokin Nijeriya.

Yayin da ya ke jawabi a wajen taron kaddamar da sabbin bindigogin jiragen ruwa biyu da hukumar kwastam ta yi a Lagos, Monguno ya ce ‘yan Nijeriya da dama sun mutu sakamakon muggan makaman da ake fasa-kwaurin su.
Ya ce gwamnatin tarayya ba za ta saduda a kan duk wata makarkashiya ko matsin lamba daga kowace kungiya ko mutane akan rufe iyakokin Nijeriya ba.
A cewar sa, wasu kasashe da ke makwaftaka da Nijeriya, sun mara wa gwamnatin tarayya baya a kan yadda za a tabbatar da tsaron iyakokin Nijeriya.
Karanta Wannan: Tsaro: Rundunar Yan Sanda Ta Ceto Mutane 22 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Imo
Munguno,
ya ce shirin Operation Swift Response da ke gudana yanzu haka a iyakokin Nijeriya
ya na samun nasara sosai, inda ya bada tabbacin cewa gwamnati ta jajirce domin
tallafa wa duk hukumomin tsaro domin ba su damar yin maganin masu hannu a fasa-kwauri.
You must log in to post a comment.