Home Labaru Masu COVID-19 sun karu zuwa 238

Masu COVID-19 sun karu zuwa 238

815
0

Cibiyar Dakile Cututtuka ta Najeriya NCDC, ta ce an samu karin mutum 6 da suka kamu da cutar ta COVID-19 a daren Litinin.

Karin wadanda suka kamu da cutar coronavirus din sun hada da mutum 2 a jihar Kwara, 2 a Jihar Edo, 1 a Jihar Ribas da kuma mutum 1 a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Cibiyar ta ce kawo yanzu mutum 238 ne suka kamu da cutar a Najeriya.

Daga cikinsu an sallami mutum 35 da suka warke daga asibiti, wasu mutum 5 sun mutu.

Hakan ke nuna zuwa yanzu mutum 198 ke kwance a cibiyoyin killace masu cutar COVID-19 a fadin Najeriya.

Adadin masu cutar COVID-19 a jihohin da ke fadin Najeriya sun hada da:

Legas – 120
Abuja – 48
Osun – 20
Oyo – 9
Edo – 11
Bauchi – 6
Akwa Ibom – 5
Kaduna – 5
Ogun – 4
Enugu – 2
Ekiti – 2
Rivers – 2
Benue – 1
Ondo – 1
Kwara – 2

Leave a Reply