Kwamitin zartarwa na gwamnatin tarayya, ya amince da fara wani wani sabon tsari da zai samar da aikin yi ga matasan Nijeriya da ke tsakanin shekaru 18 zuwa 25.
Ministan kasafi da tsare-tsare Udoma Udo Udoma ya sanar da haka, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa ta kasa da shugaba Buhari ya jagoranta. Ministan ya ce, za a ba matasa 12,000 da su ka kammala karatu amma ba su samu aiki ba, wadanda za a ba horo a kan sarrafawa da gyaran na’urori masu kwakwalwa da kayan da ke amfani da wutar lantarki daban-daban.
You must log in to post a comment.