Home Home Kididdiga: An Sace Fiye Da Dalibai 1,500 A Nijeriya – Amnesty

Kididdiga: An Sace Fiye Da Dalibai 1,500 A Nijeriya – Amnesty

107
0
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty ta ce, shekaru takwas bayan kungiyar Boko Haram ta sace ‘yan matan makarantar Chibok 276, sama da dalibai dubu 1 da 500 wasu kungiyoyi su ka sace.

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty ta ce, shekaru takwas bayan kungiyar Boko Haram ta sace ‘yan matan makarantar Chibok 276, sama da dalibai dubu 1 da 500 wasu kungiyoyi su ka sace.

Amnesty International ta bayyana haka ne a cikin wani rahoto da ta wallafa a shafin ta na yanar gizo, inda ta ce a cikin dalibai 276 na Chibok da aka sace, an kashe 16 kuma har yau ba a san inda 109 su ke ba.

Kungiyar ta kara da cewa, an sace dalibai dubu 1 da 500 a cikin watanni 22 ne, kuma har zuwa wannan lokacin akwai dalibai kimanin 120 da ke hannun wadanda su ka sace su.

Daga cikin dalibai 102 da aka sace a makarantar gwamnatin tarayya ta Birnin Yauri, har yanzu 9 su na hannun ‘yan bindiga, sannan ba a sako daya daga cikin daliban makarantar Bethel Baptist ta Kaduna da aka sace ba.