Home Labarai Kasafi: Gwamnati Za Ta Mika Wa Majalisun Dokoki Naira Tiriliyan 47 Da...

Kasafi: Gwamnati Za Ta Mika Wa Majalisun Dokoki Naira Tiriliyan 47 Da Miliyan 900

197
0
Atiku Bagudu, Shugaban Gwamnonin, APC
Atiku Bagudu, Shugaban Gwamnonin, APC

Majalisar zartaswar Najeriya ta amince da kasafin kuɗi na 2025 da ya kai naira tiriliyan 47.9.

Ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare, Atiku Bagudu ne ya bayyana haka bayan kammala taron majalisar da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta.

Ya ce kasafin kuɗin ya ƙunshi manyan ayyuka da kuma na musamman da za a gudanar a faɗin ƙasa inda za a miƙa shi gaban majalisar dokoki ta ƙasa domin yin nazari da kuma amincewa da shi.

Ya ce an yi hasashen samun bunƙasar yawan kayayyakin da ake samarwa a cikin gida da kashi 4.6 cikin 100.

Leave a Reply