Yawan masu cutar coronavirus a Najeriya ya karu da mutum 4.
Cibiyar Hana Yaduwar Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta ce sabbin masu cutar sun hada da mutum 3 a jihar Ogun da mutum 1 a jihar Osun.
NCDC ta ce karuwar masu cutar da mutum 4 ya sa yawan masu cutar a Najeriya karuwa zuwa mutum 135.
Cibiyar a sanar da haka ne ta shafinta na Twitter kamar yadda aka saba a ranar Talatan nan.