Home Labarai Kada Kuri’a Daga Ketare: Ƙudurin Zaɓe Dake Gaban Majalisa Ya Tsallake Karatu...

Kada Kuri’a Daga Ketare: Ƙudurin Zaɓe Dake Gaban Majalisa Ya Tsallake Karatu Na Biyu

253
0
Nigeria House of Representatives REPS
Nigeria House of Representatives REPS

Ƙudirin da zai yi wa kundin tsarin mulkin Najeriya kwaskwarima domin ba ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓe ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai a yau Laraba.

Ƙudirin wanda shugaban majalisar, Abbas Tajudeen da Sodeeq Abdullahi suka ɗauki nauyin sa, na neman yin gyara ga dokar zaɓe ta 2022 domin a bayar da dama ga ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje su kaɗa ƙuri’a.

An amince da karanta ƙudurin karo na biyu a watan Yuli, kuma an miƙa shi ga kwamitin da ke kula da harkokin zaɓe don ci gaba da nazarin sa.

Sai dai bayan tsallake karatu na biyu a ranar Talata, an miƙa shi ga kwamitin gyaran kundin tsarin mulki don ci gaba da tattaunawa a kan sa.

Leave a Reply