Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gana da wakilan shugabannin kungiyoyin ‘yan Nijeriya mazauna kasar Japan, yayin halartar taron kasa da kasa a kan ci-gaban kasashen nahiyar Afrika karo na bakwai da ke gudana a birnin Yokohama.
Buhari ya bayyana cewa, ya amince da cewar akwai wasu ‘yan Nijeriya da ke aikata miyagun laifuffuka a kasashen ketare,yana mai cewa irin wadannan batagarin ba wakilan kasa nagari neba.
Kalaman shugaba Buhari dai su na zuwa ne, a daidai lokacin da gwamnatin kasar Amurka ta kama wasu ‘yan Nijeriya 80 da laifuffukan zamba da damafara.
Shugaba Buhari, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na yaki da aikata miyagun laifuffuka a gida da waje, yayin da ya bukaci ‘yan Nijeriya mazauna kasar Japan su zama jakadun kasa nagari tare da yin biyayya ga dokokin kasar da suke zaune.
You must log in to post a comment.