Home Labaru Kiwon Lafiya Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Zagaye Na Uku Na Riga-Kafin Korona

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Zagaye Na Uku Na Riga-Kafin Korona

177
0

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa za ta ƙaddamar da riga-kafin korona zagaye na uku a ranar Juma’a mai zuwa.

Jaridar Punch ta ruwaito daraktan lafiya a matakin farko na ƙasa, Dakta Faisal Shuaib na sanar da hakan yayin ƙaddamar da riga-kafin a sansanin ƴan gudun hijira dake Abuja.

Shuaib ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta yanke shawarar amfani da rigakafin korona na Kamfanin Pfizer Bio-N-tech a zagaye na ukun.

Tuni dai wasu ƙasashen duniya suka soma riga-kafin zagaye na uku domin ƙara ƙarfin riga-kafin a jikin waɗanda aka yi wa zagayen farko da na biyu.