Wakilan gwamnatin tarayya sun gana da shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya, a kan aiwatar da sabon tsarin mafi karancin albashin Naira 30,000 da kuma yin gyara a albashin ma’aikatan gwamnati.
An dai fara ganawar ne, jim kadan bayan isowar ‘yankungiyar a ma’aikatar kwadago da daukar ma’aikata a Abuja da ke Abuja.
Da ya ke jawabin sa, ministan kwadago Chris Ngige, ya ba shugabannin kungiyar tabbacin cewa zai cigaba da kasancewa a tsaka-tsaki a tattaunawar, tsare da yaba wa ‘yan kungiyar bisa nuna fahimta da su ka yi.
Ngige ya sanar da cewa, za a sake wani zama tare da shugabannin hukumomin gwamnati, domin tattaunawa a kan albashin da za a iya biyan ma’aikata.
Da
farkon zaman an hana ‘yan jarida daukar rahoton ganawar da aka yi cikin sirri,
amma daga bisani sai ministan ya ba su damar shiga.
You must log in to post a comment.