Home Labaru Gwamnatin Tarayya Ta Gana Da Shugabannin Kungiyar Kwadago A Abuja

Gwamnatin Tarayya Ta Gana Da Shugabannin Kungiyar Kwadago A Abuja

912
0
Tsarin IPPIS: Yajin Aiki Kungiyar ASUU Haramtaccene - Ngige
Tsarin IPPIS: Yajin Aiki Kungiyar ASUU Haramtaccene - Ngige

Wakilan gwamnatin tarayya sun gana da shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya, a kan aiwatar da sabon tsarin mafi karancin albashin Naira 30,000 da kuma yin gyara a albashin ma’aikatan gwamnati.

An dai fara ganawar ne, jim kadan bayan isowar ‘yankungiyar a ma’aikatar kwadago da daukar ma’aikata a Abuja da ke Abuja.

Da ya ke jawabin sa, ministan kwadago Chris Ngige, ya ba shugabannin kungiyar tabbacin cewa zai cigaba da kasancewa a tsaka-tsaki a tattaunawar, tsare da yaba wa ‘yan kungiyar bisa nuna fahimta da su ka yi.

Ngige ya sanar da cewa, za a sake wani zama tare da shugabannin hukumomin gwamnati, domin tattaunawa a kan albashin da za a iya biyan ma’aikata.

Da farkon zaman an hana ‘yan jarida daukar rahoton ganawar da aka yi cikin sirri, amma daga bisani sai ministan ya ba su damar shiga.