Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar mutane uku da su ka hada da wani magidanci da matar sa da kuma ‘yar su, sakamakon gobarar da ta afku a gidan su da ke Gayawa-Tsohuwa a karamar hukumar Ungogo.
Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana ta jihar Kano Saidu Mohammed, ya ce wadanda su ka mutun sun hada da yarinya ‘yar shekaru biyu.
Ya ce sun samu kiran waya daga wani mutum mai suna Malam Mudassir Abdullahi, da misalin karfe 3:57 na safiyar Larabar da ta gabata, cewa gobara ta tashi a wani gida.
Mudassir
Abdullahi, ya ce nan da nan su ka tura ma’aikatan su da kayan aiki domin kashe
wutar, sai dai bayan an garzaya da mutanen zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad
ne likitoci su ka tabbatar da mutuwar su.