Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna, ya bada umurnin rufe duk tashoshin saida iskar gas da ke wuraren zaman jama’a a fadin jihar.
El-Rufa’i, ya kuma roki mazauna jihar su kai rahoton wurarren da ake saida Gas a cikin jama’a ba tare da bata lokaci ba domin daukar matakin gaugawa.
Gwamnan, ya ce tashar gas na da hatsari sosai, wanda ya kamata a rika gudanar da harkar ne a wuraren kasuwanci, inda za a iya daukar matakan kariya.
El-Rufa’i,
ya kuma kai ziyarar jaje ga iyalan Farfesa Simon Mallam, wanda ya rasa ran sa biyo
bayan fashewar tukunyar Gas a unguwar Sabon Tasha da ke garin Kaduna, sannan ya
ziyarci mutanen da lamarin ya shafa a babban asibitin St Gerald da ke Kaduna.