Home Labaru Dimokradiyya: INEC Ta Bayyana Ranakun Zaben Gwamnan Jihohin Bayelsa Da Kogi

Dimokradiyya: INEC Ta Bayyana Ranakun Zaben Gwamnan Jihohin Bayelsa Da Kogi

217
0
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta kasa, INEC
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta Kasa, INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kan ta ta Kasa INEC, ta ce za ta gudanar da zaben gwamna a jihohin Bayelsa da Kogi a ranar 2 Ga Nuwamba na shekara ta 2019.

Kakakin Yada Labarai na hukumar zabe ta kasa Festus Okoye ne ya bayyana haka a Abuja.

Ya ce bayan Shugabannin INEC sun gudanar da taro, hukumar ta fito da jadawalin yadda zabubbukan za su kasance, tun daga zaben fidda-gwani har zuwa na gama-gari.

Hukumar zaben ta ce za ta fitar da sanarwar fara hada-hadar zaben a ranar 1 ga watan Agusta, kuma duk jam’iyyar da ke sha’awar shiga takara za ta yi zaben fidda-gwani tsakanin ranar 2 zuwa 29 ga watan Agusta.

Haka kuma, hukumar ta ce ta na bukatar duk jam’iyyar da za ta shiga zaben ta aika da sunayen wakilan ta zuwa ranar 2 ga Oktoba.

INEC ta ce a cikin watan Mayu za ta yi gagarimin aikin nazari da kuma bin diddigin yadda zaben 2019 ya gudana.