Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya dakatar da shirin da Ministar kudi Zainab Ahmed da Ministan Shari’a Abubakar Malami su ka kitsa don ya amince a fara ɗibar kuɗaɗen jihohi ana biyan wasu ‘yan kwangila, alhalin rikicin biyan kuɗin ya na kotu ba a kai ga yanke hukunci ba.
Wata majiya ta ce, a wajen taron Majalisar Zartaswa ta kasa na ranar 3 Ga Agusta ne, shugaba Buhari ya bada umarnin kada a fara cirar kuɗin bayan ya riga ya sa hannun amincewa a baya.
A baya dai rahotanni sun Ambato yadda Gwamnonin Nijeriya su ka rubuta wa Shugaba Buhari wasiƙar rashin amincewar su a kan fara cirar kuɗaɗen.
Yanzu haka dai ana cikin tafka shari’a a kotu, kuma kotun Ƙoli ta bada umarnin kada a fara cirar kuɗaɗen sai an kammala shari’a tsakanin masu dillancin kwangilar da ake rigima da su tukunna.
Yayin da Ministoci su ka hallara a wajen taron Majalisar Zartarwa ta kasa, sai Ministar kudi da Abubakar Malami su ka bijiro da batun cewa Shugaba Buhari ya gaggauta amincewa a fara biyan kuɗaɗen kawai.














































