Home Labarai Bangladesh : Shugaba Ya Yi Kiran Da a Kai Zuciya Nesa

Bangladesh : Shugaba Ya Yi Kiran Da a Kai Zuciya Nesa

233
0
OIP (4)
OIP (4)

Shugaban ya yi kira ga samun hadin kan addinai bayan ganawa da mahaifiyar dalibar da ‘yan sanda suka harbe har lahira,

lamarin da ya janyo zanga-zangar da ta kawo karshen mulkin Sheikh Hasina na tsawon shekaru 15.

Yunus mai shekaru 84, da ya taba lashe lashe kyautar Nobel, ya dawo daga Turai a wannan makon don jagorantar gwamnatin wucin gadi,

da ke fuskantar babban kalubale na kawo karshen rikice-rikice da aiwatar da sauye-sauyen demokradiyya.

Hare-haren ramuwar gayya da aka kai kan mabiya addinin Hindu tsiraru a kasar tun bayan hambarar da gwamnatin Hasina,

ya haifar da fargaba a makwabciyar kasar Indiya da kuma fargaba a cikin gida.

A yayin wata ziyara da ya kai birnin Rangpur da ke arewacin kasar, Yunus ya yi kira da a kwantar da hankali,

ta hanyar tunawa da karrama Abu Sayeed, dalibi na farko da aka kashe a rikicin na watan jiya.

Leave a Reply