Tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, wanda aka sauke daga gadon sarauta a ranar Litinin, ya yi jawabin bankwana ga al’ummar jihar Kano baki daya.
Mai martaban mai baringado ya godewa al’ummar bisa hadin kan da suka ba shi lokacin da yake kan karagar mulki.
Sarki Sanusi II, ya yi jawabinne a wani daki da ke fadarsa jim kadan kafin a fitar da shi zuwa jihar Nasarawa inda zai zauna na wani lokaci.














































