Home Labaru Arewa Maso Gabas: Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Nadin Mukaman Buhari

Arewa Maso Gabas: Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Nadin Mukaman Buhari

220
0

Majalisar Dattata tabbatar da Manjo Janar Paul Tarfa mai ritaya da sauran zababbun ‘yan kwamitin habaka ci-gaban Arewa maso Gabas da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada.

Rahotanni sun bayyana cewa, Manjo Janar Tarfa zai jagoranci kwamitin tabbatar da habaka ci-gaban yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Majalisar dattawa ta yi na’am da nadin mukaman shugaban Buhari, yayin shugaban kwamitin bincike a kan nadin mukamai na ayyukan musaman Sanata Abdul’aziz Nyako ya gabatar da sakamakon sa.