Hukumar daƙile yaduwar cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC, ta ce karin mutum 618 ne suka kamu da cutar korona a faɗin Najeriya a ranar Juma’a, haka kuma cutar ta yi ajalin wasu mutum 10.
Hukumar ta ce akasarin waɗanda suka kamu a jihar Lagos suke, inda aka samu mutum 312 dauke da cutar, yayin da a Akwa Ibom aka samu 89.
Jerin jihohin da aka samu bullar cutar ranar Juma’ar sun kunshi Lagos-312, Akwa Ibom-89, Edo-71, Rivers-41, Ekiti 20, Plateau-20, Delta-15, Kwara-14, FCT-11, Osun-8, Oyo-4, Ogun-3, Benue-3, Gombe-1, Kaduna-1
Jumillar adadin mutanen da suka kamu a faɗin ƙasar sun kai 190,333, sai dai 169,815 sun warke.
Akwai kuma mutum 2,308 da suka mut