Home Addini Ana Ci Gaba Da Jigilar Maniyyatan Najeriya Zuwa Sa’udiyya

Ana Ci Gaba Da Jigilar Maniyyatan Najeriya Zuwa Sa’udiyya

250
0
Pilgrims heading for Hajj4
Pilgrims heading for Hajj4

NAHCON na ci gaba da jigilar maniyyatan zuwa ƙasa mai tsarki domin sauke farali a bana.

Ta wallafa a shafinta na X, zuwa yau Asabar da safe jirage 12 ne ɗauke da maniyyatan suka isa Saudiyya.

Hukumar ta ce 11 daga cikin jiragen sun sauka ne a birnin Madina, yayin da ɗaya kuma ya sauka a Jedda.

NAHCON ta ce daga cikin adadin Da suka isa ƙasa mai tsarkin 2934 maza ne, yayin da 2140 mata ne.

A makon nan NAHCON ta fara jigilar maniyyatan, inda aka fara da jihohin Kebbi,Bauchi,Nasarawa,Legos da Abuja.

Leave a Reply